Friday, May 4, 2018

WATA KISSA, ALOKACHIN KHALIFANCHIN SAYYIDINA UMAR BIN KHATTAB

KARANTA KACI WATA KISSA A LOKACIN SAYYIDINA UMAR ALLAH R.A


A zamanin khalifa Umar dan Khattaab, wasu mutane uku suka zo masa suna rike da wani saurayi suka ce:
Ya Amiral muminina! Wannan mutum ya kashe mana mahaifinmu.


Umar: kai don me ka kashe musu uba?


Saurayi: Ni makiyayi ne, rakumata ce ta ci itaciyar gonar mahaifinsu, sai mahaifinsu ya bugi rakumin da dutsi, rakuma ta mutu, ni kuma na dauki dutsin na buge shi
ya mutu.


Umar: saboda haka zan tsaida haddi akan ka.


Saurayi: ka saurara min kwana uku, mahaifina ya mutu ya bar ni da kanwata da
kuma dukiya, idan ka kashe ni, dukiyar da yar uwata za su tozarta.


Umar: wa zai lamunce ka?


Saurayi ya duba cikin mutane sai ya nuna Sahabi "Abu Dhar".


Umar: ka lamunce masa Ya Aba Dharr?


Abu Dharri: na'am


Umar: ba ka san mutum ba ka lamunce, to idan ya gudu haddi zai koma kanka.


Abu Dharr: na yarda.


Saurayi ya tafi, aka kwana biyu, an shiga na uku, saurayi bai zo ba,


Hankalin kowa ya tashi akan Abu Dharri kar haddi ya koma kansa.


Kafin sallar magariba sai ga saurayi ya zo a gajiye, ya tsaya a gaban khalifa Umar.


Saurayi: na mika dukiyar ga kawuna yanzu ina hanunka, ka tsaida haddi a kaina.


Cikin mamaki Umar ya ce: me ya dawo da kai, bayan ka sami damar da za ka
iya gudu abinka?


Saurayi: na ji tsoro, kar a ce cika alkawari ya kare cikin mutane.


Umar ya juya ga Abu Dharr: me ya sa ka lamunce masa?


Abu Dharr: na ji tsoro, kar a ce alheri ya Kare cikin mutane.


Wannan jawabi ya yi tasiri ga masu Neman jinin ubansu, suka ce sun yafewa
saurayi.


Umar: don me?


Suka ce: muna tsoro, kar a ce afuwa ta Kare a cikin mutane.


Ni ma na isar muku da wannan kissa ne don ina tsoron kar a ce kira/tunatarwa zuwa ga aikata alkhairi (wato da'awa) ya Kare cikin mutane. Da fatan za mu kasance masu:
Cika alkawari, alkhairi da kuma Afuwa ga junanmu.
ADMIN: ADAM MOHD ADAM GAYA



1 comment: